in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Najeriya ta yi kiran da a yiwa dokokin biyan haraji a nahiyar Afirka gyaran fuska
2017-09-27 09:06:42 cri
Gwamnatin Najertiya ta bayyana kudurinta na jagorantar kamfel din da ake yi game da yiwa dokokin biyan haraji a nahiyar Afirka gyaran fuska, saboda alaka mai karfi dake tsakanin harkar raya tattalin arziki da batun da ya shafi biyan haraji.

Ministar kudin Najeriya Kermi Adeosun wadda ta bayyana hakan yayin da take jawabi a taron kasa da kasa na yini biyu game da biyan haraji a Afirka, wanda ya gudana a Abuja, fadar mulkin kasar, ta ce babu wata kasa mai wadata da take da tsarin biyan haraji mai rauni, haka kuma babu matalauciyar kasa mai nagartaccen tsarin biyan haraji. A don haka, akwai bukatar a bullo da tsarin biyan haraji mai inganci wanda zai tabbatar da cewa, kudade haraji na shiga lalitar gwamnati yadda ya kamata.

Bugu da kari, ministar ta ce akwai bukatar bangaren majalisa da na shari'a a nahiyar su ba goyan bayan don ganin an hukunta masu kin biyan haraji. Tana mai cewa, yanzu Najeriya ce kurar baya a duniya, inda bangaren harajinta ke tallafawa GDPn kasar da kaso 6 cikin 100 kawai.

An shirya taron ne da nufin inganta matakan biyan haraji a nahiyar Afirka, ta hanyar musayar bayanai, ilimantar da jama'a, samar da horo, bayar da gudummawa ga ajandar biyan haraji a shiyyar da ma duniya baki daya. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China