in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Warware batun nukiliya a duniya lamari ne dake bukatar hadin kan kasa da kasa, in ji jami'in MDD
2017-09-27 16:44:46 cri
Sakatare-janar na MDD Antonio Guterres ya bayyana a jiya Talata cewa, batun raba duniya da makaman nukiliya lamari ne dake neman daukin kasa da kasa.

Da yake jawabi a wani babban taron MDD domin tunawa da ranar kawar da makaman nukiliya na kasa da kasa, wanda aka saba gudanarwa a ranar 26 ga watan Satumba na kowace shekara, mista Guterres ya bayyana cewa, duniya za ta zauna lafiya ne kadai idan ya kasance ta kauracewa amfani da makaman nukiliya baki daya a doron duniya.

Ya ce kasashen duniya wadanda suka mallaki makaman nukiliya suna da wani nauyi na musamman dake rataye a wuyansu, ta hanyar daukar kwararan matakai, ciki har da yarjejeniyoyin da aka cimma a tarurrukan karawa juna sani game da shirin dakile bazuwar makaman nukiliyar wato (NPT) a takaice. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China