Taron da ya gudana tsakanin ranakun 19 da 25 ga watan nan, ya samu halartar shugabanni da wakilai na kasashe da gwamnatoci 196, inda kuma suka gabatar da jawabai.
Adadin wadanda suka gabatar da jawabi a taron na wannan karon ya kasance mafi yawa cikin shekaru 11 da suka gabata.
Bugu da kari, an yi taron shawarwari na musamman kan batun sauyin yanayi da kuma taron kwamitin sulhu na MDD kan gudanar da ayyukan kiyaye zaman lafiya da dai sauransu. (Maryam)