in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Nijeriya ta ayyana kungiyar 'yan aware ta kasar a matsayin ta 'yan ta'adda
2017-09-16 12:43:27 cri
Gwamnatin Nijeriya ta ayyana kungiyar masu rajin kafa jamhuriyar Biafra ta IPOB a matsayin kungiyar 'yan ta'adda, tana mai bukatar iyaye su hana yaransu shiga cikinta.

Cikin wata sanarwar da ta fitar a jiya Jumma'a, kakakin ma'aikatar harkokin tsaron Nijeriya Manjo Janar John Enenche, ya ce bayan nazarin kwararru da abubuwan da suka faru a baya bayan nan, ya zama tilas a bayyanawa al'umma cewa, ikirarin da masu fafutukar ke yi na cewa kungiyarsu ba ta rikici ba ce, karya ne.

Sanarwar ta ce wasu daga cikin ayyukan kungiyar sun hada da kafa hukumar liken asiri ta Biafra da ikirarin kafa dakarun kasar Biafra da kuma toshe wasu hanyoyin jama'a da karbar kudi daga mutanen da ba su ji, ba su gani ba a haramtattun shingayen bincike.

Sauran sun hada da mallaka da amfani da makamai ciki har da duwatsu da adduna da fasassun kwalabe a kan soji dake sintiri a ranar 10 ga wannan watan.

Manjo Janar Enenche ya kara da cewa, kungiyar ta kuma yi fito na fito da sojoji a wani shingen bincike a ranar 11 ga watan nan, inda kuma suka yi yunkurin kwace bindigoginsu.

Rundunar tsaron Nijeriya dai na mai tabbatarwa al'ummar kasar cewa, bisa kuduri zuwa shiri da manufarta kamar yadda aka nazarta, kungiyar IPOB ta tsagerun 'yan ta'adda ce. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China