in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilin Sin : An doshi warware batun Syria ta hanyar siyasa
2017-09-25 13:53:11 cri
Manzon musamman na kasar Sin kan batun Syria Xie Xiaoyan ya yi kira da a kara yin hadin gwiwa da kasar Masar a kokarin da ake na warware rikicin kasar ta Syira, a daidai gabar da aka kama hanyar warware batun Syriar ta hanyar siyasa.

Jami'in na Sin wanda ya bayyana hakan ga manema labarai bayan ganawarsa da mataimakin ministan harkokin wajen kasar Masar mai kula da harkokin kasashen Larabawa Tarek Al-Kouni. Ya ce sun fahimce wasu kasashe sun canza matsayinsu game da batun Syria, wannan wata kyakkyawar dama ce ta warware batun ta hanyar siyasa.

Xie ya ce, matakan da masu ruwa da tsaki a wannan batu suka dauka na amincewa su kafa shiyoyin tsaro, alama ce dake nuna cewa, al'ummomin kasa da kasa suna fatan bangarorin da wannan rikici ya shafa, za su yi kokarin warware bambance-bambance dake tsakaninsu, ta yadda za su hanzarta bullo da matakan siyasa don kawo karshen wannan takaddama. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China