in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD za ta yi sabon zaman tattaunawar zaman lafiya kan rikicin Syria a 10 da watan Yuli
2017-06-18 12:29:51 cri
Wakilin musamman na MDD kan rikicin Syria Staffan de Mistura ya sanar a ranar Asabar cewa, yana fatan ayyana sabon zagaye na zaman tattaunawa kan warware rikicin Syria a Geneva a ranar 10 watan Yuli.

Ya bayyana hakan ne cikin wata sanarwa, inda aka bayyana cewa, ana bukatar mahalarta taron da aka gayyata za su hallara a ranar 9 watan Yulin domin tattaunawar a washe gari wato 10 ga watan.

De Mistura ya kara da cewa ya sake amincewa da kiran zagaye na gaba na tattaunawar a watannin Augusta da Satumba, kuma kamar yadda aka saba gudanarwa a sauran zagayen tarukan na lokutan baya, za'a gabatar da takardun gayyata ne bisa ga doka ta 2254 da MDD ta tanada.

Sanarwar ta kara da cewa, baya ga tattaunawar da za'a gudanar da bangarorin kasar ta Syria a hukumance, za kuma a gudanar da taron tuntuba da kwararru domin tsara daftarin dokoki da batutuwan shari'a a zagayen karshe na tattaunawar da aka gudanar, domin bada damar ci gaba da tattaunawar zaman lafiyar don rikicin na Syria. (Ahamd Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China