in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Dakarun gwamnatin Sham sun kwace wani muhimmin sansanin kungiyar IS dake lardin Aleppo
2017-06-05 13:10:16 cri
Rundunar sojan kasar Sham ta shelanta jiya Lahadi, cewa a wannan rana dakarun gwamnatin kasar sun kwace garin Maskanah, wani muhimmin sansanin kungiyar IS dake gabashin lardin Aleppo na kasar.

A wannan rana, kungiyar sa ido game da kare hakkin al'ummar Sham, wadda hedkwata a birnin London na kasar Britaniya ta ce, garin Maskanah shi ne sansanin karshe na kungiyar IS dake lardin Aleppo.

Bayan da dakarun gwamnatin Sham ta kwace birnin Aleppo, fadar lardin Aleppo a watan Disambar bara, dakarun gwamnatin sun kuma kwace yankunan masu tarin yawa a gabashin lardin sakamakon matakan sojan da suka aiwatar da nufin farautar kungiyar ta IS a lardin.

A 'yan watannin baya, dakarun sojan Sham sun sha daukar matakan soja da nufin kawar da sansanonin kungiyar IS dake cikin kasar. A yayin da dakarun gwamnatin take farautar kungiyar IS, ita kuma kungiyar sojojin sa-kai dake fafutukar wanzar da dimokuradiyya ta Sham wadda ke karkashin jagorancin Kurdawa ita ma tana kokarin yiwa garin Rakka wato hedkwatar kungiyar IS a kasar Sham kawanya. (Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China