in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jamus zata tusa keyar masu neman mafaka a kasar
2016-12-24 13:22:13 cri
Shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel, ta sanar a jiya Juma'a cewa, gwamnatin kasar tana kokarin mayar da masu neman mafaka a kasar, domin samar da ingantaccen tsaro a kasar baki daya.

Merkel ta bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa, bayan an tabbatar da cewa Anis Amri, dan kasar Tunisiya wanda ake zargi da kaddamar da harin kasuwar sayar da kayayyakin kirsimeti a birnin Berlin, cewar an kashe shi, kuma jami'an yan sandan kasar Italiya ne suka harbe shi a lokacin wani sintiri a Milan da safiyar jiya Juma'a.

Harin na kasuwar kirsimetin ya haifar da tambayoyi iri iri, Angela Merkel ta bayyana cewa gwamnatinta a shirye take ta dauki dukkan matakan da suka dace domin tabbatar da tsaron kasar.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China