in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ministan tsaron Jamus ta karyata maganar Trump ta wai kasar Jamus ta ci bashi ga NATO
2017-03-20 13:08:42 cri
Jiya Lahadi kafofin watsa labaru na kasar Jamus sun bayyana cewa, ministar tsaron kasar Ursula von der Leyen, ta yi watsi da kalaman shugaba Trump na Amurka, game da cewar sa wai Jamus ta ci bashin kudi da yawa daga kungiyar tsaro ta NATO. Tana mai cewa, wannan maganar ta Trump ba gaskiya ba ce.

A ranar 18 ga wata ne dai shugaba Trump ya rubuta wani sako a dandalin sada zumunci, yana mai cewa, kasar Jamus ta ci bashi da yawa daga NATO, kuma Amurka na samar da tsaro mai nagarta da tsadar gaske ga kasar ta Jamus, don haka kamata ya yi Jamus ta saka mata.

Ministar ta ce, NATO ba ta ajiye kudin da za a ci bashi, kuma kasar Jamus ta yi alkawarin kara kasafin kudin tsaron ta da kashi 2 cikin dari bisa GDPn ta, amma ba daidai ba ne an hada wannan hasashe da kungiyar NATO. Ta ce, za a yi amfani ne da kasafin kudin tsaron na Jamus, wajen ayyukan kiyaye zaman lafiyar MDD, da na murkushe ta'addanci da dai sauransu. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China