Wang Yi, wanda ke Jamus domin halartar muhimmin taro tsakanin kasar Sin da Jamus kan harkokin diflomasiyya da tsaro, ya bayyana haka ne yayin wani taron manema labarai na hadin gwiwa tsakaninsa da mataimakin shugaban Gwamnatin Jamus kuma Ministan harkokin wajen kasar Sigmar Gabriel.
Ya ce taron G20 da zai gudana a Hamburg, zai dora ne a kan nasarorin da aka samu yayin taron da aka yi a bara a Hangzhou na Kasar Sin, tare da ci gaba da kokarin habaka tattalin arzikin duniya. (Fa'iza Mustapha)