in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta ce ya kamata a yi koyi da sanarwar da aka fitar shekaru 12 da suka gabata wajen daidaita matsalar Koriya ta Arewa
2017-09-19 21:09:15 cri
Mai magana da yawun ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin, Lu Kang, ya bayyana yau Talata cewa, wata sanarwar da aka fitar a ranar 19 ga watan Satumban shekara ta 2005, wato shekaru 12 da suka shige, za ta iya zama abar koyi wajen warware matsalar Koriya ta Arewa a halin yanzu.

Idan an dubi tarihi, za'a fahimci cewa, daga ranar 26 ga watan Yuli zuwa ranar 7 ga watan Agusta, kana, daga ranar 13 zuwa 19 ga watan Satumba na shekara ta 2005, Sin da Koriya ta Arewa da Japan da Koriya ta Kudu da Rasha tare kuma da Amurka sun gudanar da shawarwari zagaye na hudu a birnin Beijing, inda suka fitar da wannan sanarwa da ake kira sanarwar ranar 19 ga watan Satumba.

A cikin wannan sanarwa, Koriya ta Arewa ta yi alkawarin cewa, za ta yi fatali da duk wani makamin nukiliya da ta mallaka gami da shirinta na kera makaman nukiliya, ita kuma Amurka ta ce, ba za kaiwa Koriya ta Arewa harin nukiliya ba.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China