in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Koriya ta Arewa ta yi kashedi ga Amurka cewa za ta mayar da martani idan Amurka ta kara saka mata takunkumi
2017-09-11 15:40:51 cri
Ma'aikatar harkokin wajen kasar Koriya ta Arewa ta fitar da sanarwa a yau Litinin cewa, idan har kasar Amurka ta nemi kwamitin sulhun MDD ta kara saka mata takunkumi, to ita ma kasar Koriya ta Arewa za ta mayarwa Amurkar martani

Sanarwar ta bayyana cewa, Koriya ta Arewa tana inganta shirinta na raya makaman nukiliya ne domin takawa manufofin kasar Amurka na nuna kiyayya da barazanar makaman nukiliya, ta yadda za ta dauki matakan kare kanta.

Rahotanni na cewa, kasar Amurka ta tsara wani sabon daftarin sakawa Koriya ta Arewa takunkumi sakamakon gwajin nukiliya da Koriya ta Arewa ta yi a ranar 3 ga wata, kuma yau ne ake sa ran za a kada kuri'u kan daftarin a yayin zaman kwamitin sulhun MDD.

A farkon watan Agusta, kwamitin sulhun MDD ya zartas da kuduri mai lamba 2371 game da batun nukiliya na zirin Koriya, kana ya yi Allah wadai da harba makamai masu linzami da za a iya harba su daga wata nahiya zuwa wata da kasar Koriya ta Arewa ta yi a ranakun 4 da kuma 28 ga watan Yuli, inda ya bukaci kasar Koriya ta Arewa da ta yi watsi da shirinta na makaman nukiliya da kuma makamai masu linzami, kana ya yanke shawarar saka mata karin takunkumi. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China