in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Barkewar cutar kwalara a sansanin 'yan gudun hijira ya yi sanadin mutuwar mutane 8 a Nijeriya
2017-09-04 08:50:31 cri
Ma'aikatar lafiya ta jihar Borno dake arewa maso gabashin Nijeriya, ta tabbatar da mutuwar mutane 8 sakamakon barkewar cutar kwalara a sansanin 'yan gudun hijira dake Maiduguri, babban birnin jihar.

Kwamishinan lafiya na jihar Haruna Mshelia, ya ce gwamnati ta shirya wani asibiti mai gadaje 30 domin inganta kula da mutane tare da takaita yaduwar cutar.

Kungiyar likitocin agaji ta duniya MSF ta ce cutar da ta barke a sansanin Muna Garage na birnin Maiduguri, ta tsananta ne sanadiyyar ambaliyar ruwa kamar da bakin kwarya da aka yi makonni 3 da suka gabata ta haifar.

Shugabar Kungiyar a birnin Maiduguri Ann Cillers, ta ce jimilar mutane 200 ne aka kwantar a asibiti tun farkon barkewar cutar, inda aka sallami 100 daga cikinsu.

Ann Cillers ta kara da cewa, tun daga ranar Asabar da ta gabata sama da marasa lafiya 50 aka kwantar a wani asibiti da kungiyar ke kula da shi dake wani bangare na birnin. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China