in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wani jami'i ya ce da sauran rina a kaba game da fitar Najeriya daga matsin tattalin arziki
2017-09-07 09:17:02 cri
Babban jami'in kididdiga a hukumar kididdiga ta Najeriya Yemi Kale, ya ce dole ne a yi taka tsantsan game da batun fitar kasar daga halin matsin tattalin arziki, duba da cewa har yanzu akwai gibi, a bangaren ma'aunin tattalin arziki na GDPn kasar.

Da yake zantawa da manema labarai a birnin Abuja, fadar mulkin kasar, Mr. Kale ya ce ko da yake an samu ci gaba, amma hakan bai sauya yanayin da al'ummar kasar ke ciki ba.

Ya ce Najeriya na da matakai daban daban da za ta dauka, kafin kaiwa ga matsayin da kowa zai gani a kar. Babban dalilin da ya sanya kuwa har yanzu talakawan kasar ba su fara gani a masakin su a cewar jami'in, shi ne dogaron da kasar ke yi mafi yawa, daga kudaden da ake samu daga cinikayyar danyen mai.

A ranar Talata ne dai hukumar kididdigar ta Najeriya, ta bayyana cewa kasar ta fita daga matsin tattalin arziki da ta dage bata fuskanci irin sa ba, bayan da GDPn kasar ya karu da kaso 0.55 bisa dari, a rubu'i na biyu na shekarar nan da muke ciki.

Tun a rubu'i na biyu na shekarar bara ne kasar ta dulmiya cikin halin komadar tattalin arziki, matakin da ya haifar da karin matsin rayuwa ga al'ummar kasar. (Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China