in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta samar da na'urorin hasashen yanayi na zamani ga kasar Kenya
2017-09-12 10:37:09 cri
An gudanar da bikin mika na'urorin hasashen yanayi na zamani guda 5 da kasar Sin ta samarwa kasar Kenya a birnin Nairobi, inda jakadan Sin dake kasar Kenya Liu Xianfa da Ministar kula da yanayi da albarkatun halittu ta kasar Kenya Judi Wakhungu, suka daddale yarjejeniyar mika na'urorin.

Yayin bikin na jiya, jakada Liu Xianfa ya bayyana cewa, amfani da na'urorin da kasar Sin ta samar zai kara karfafa hadin gwiwa tsakanin Sin da Kenya a fannonin hasashen yanayi da aikin gona da tinkarar sauyin yanayi da sauransu.

A nata bangare, Judi Wakhungu ta bayyana godiya ga kasar Sin bisa bayar da gudummawar, inda ta ce na'urorin da kasar Sin ta bayar kyauta sun bude wani sabon babi ga aikin hasashen yanayi a Kenya, kuma za'a girke su a sassa daban-daban na kasar, wadanda za su kunshi yankuna da dama.(Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China