in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An yi bikin mika cibiyar nazari ta hadin gwiwar Sin da Afirka a Nairobi
2016-09-27 11:04:19 cri

A jiya ne, jakadan kasar Sin dake kasar Kenya Liu Xianfa ya mika mabudin dake wakiltar cibiyar nazari ta hadin gwiwar kasashen Sin da Afirka ga jami'ar kimiyya da fasahar noma ta Jomo Kenyatta, inda aka kammala mika wannan cibiyar nazari a hukunce.

A jawabinsa yayin bikin mika cibiyar, Liu Xianfa ya bayyana cewa, cibiyar nazari ta hadin gwiwar Sin da Afirka, ita ce babbar hukumar nazari da samar da ilmi ta farko da gwamnatin kasar Sin ta gina a ketare, kuma ta kasance babbar alama ta hadin gwiwa da musaya tsakanin kasar Kenya da kasar Sin. Ya ce, yana fatan kasashen biyu za su karfafa fahimtar juna a tsakaninsu ta hanyar yin hadin gwiwa a fannin nazari, a kokarin neman ci gaba tare.

Mataimakiyar shugaban jami'ar kimiyya da fasahar noma ta Jomo Kenyatta Mabel Imbuga ta nuna godiya matuka dangane da taimakon da gwamantin Sin ta samar wa jami'ar. Ta kuma bayyana godiya matuka da fasahohin zamani da sahihiyar kawar Sin ta kawo wa kasar Kenya, inda aka gina wannan cibiyar nazari ta hadin gwiwar Sin da Afirka, tare samar da horo ta fuskar kimiyya da fasaha ga 'yan kasar, lamarin da zai samar da dama mai kyau ga kasashen biyu wajen karfafa hadin gwiwarsu a fannin yin nazari a nan gaba. Ta ci gaba da cewa, cibiyar nazarin za ta tallafa wa kasar Kenya, har ma ga dukkan kasashen Afirka baki daya. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China