in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hadin gwiwar Sin da Kenya na bunkasa tattalin arzikin Kenya, in ji wani jami'in diflomasiyyar Sin
2017-05-26 20:00:53 cri
Jami'i mai lura da harkokin tattalin arziki da cinikayya a ofishin jakadancin kasar Sin dake kasar Kenya Guo Ce, ya bayyana cewa ci gaban da ake samu game da dangantakar Sin da kasar Kenya, zai tallafawa bunkasar tattalin arzikin kasar Kenya.

Mr. Guo Ce ya yi wannan tsokaci ne cikin wani sharhi da wata jaridar kasar ta Kenya ta wallafa a Juma'ar nan, yana mai cewa kusan rabin daukancin ayyukan raya kasa guda 30, dake karkashin kudurorin kasar na samun ci gaba nan da shekarar 2030, sun samu ne sakamakon hadin gwiwar sassan biyu.

Mr. Guo ya kara da cewa, aikin layin dogo wanda kasar Sin ke daukar nauyin ginawa tsakanin biranen Mombasa zuwa Nairobi a kasar ta Kenya, shi ne aiki mai zaman kansa mafi girma da ake gudanarwa, a fannin ginin layin dogo a dukkanin gabashin Afirka.

Ya ce ya zuwa karshen shekarar bara, ginin layin dogon mai tsawon kilomita 480, ya samar da guraben ayyukan yi 42,000 ga al'ummar Kenya, ciki hadda kaso 42.3 bisa dari a fannin fasaha da na gudanarwa.

Mr. Guo ya kara da cewa, wannan layin dogo na zamani, zai baiwa Kenya damar zama a kan gaba wajen bunkasuwar sufurin jiragen kasa, wanda hakan zai mayar da ita cibiyar bunkasar tattalin arzikin ta fuskar masana'antu da cinikayya a yankin da take.(Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China