in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Somaliya za ta yi babban taro kan sauya fasalin zaben kasar
2017-07-09 12:03:05 cri
Hukumar dake shirya zaben kasar Somaliya za ta gudanar da wani babban taron kasa da kasa na kwanaki 3 domin yin nazari game da yadda kasar za ta mayar da tsarin zabenta na mutum guda kuri'a guda a lokacin zaben kasar.

Taron wanda ake fatar shirya shi tsakanin ranar 10 zuwa 12 ga wannan watan a Nairobin kasar Kenya, wanda hukumar zabe mai zaman kanta ta kasar NIEC ce za ta shirya da hadin gwiwar hukumar Arab EMBs, tare da tallafin hukumar inganta sha'anin zabe ta MDD IESG.

Wata sanarwa daga shirin raya ci gaban kasashe na MDD a Somali UNDP, ya bayyana cewa, wakilan za su tattauna batutuwa da suka shafi yin rajistar jam'iyyun siyasa, da duba hanyoyi da matakan da za'a yi amfani da su, da kuma yin musayar ilmi tsakanin kasashen Afrika da na Larabawa wadanda suka gudanar da makamancin wannan tsarin.

Sanarwar ta kara da cewa, ana fatar wannan babban taro zai taimakawa hukumar zaben kasar Somaliya wajen samun nasarar yin rajistar jam'iyyun siyasar kasar a kokarin tabbatar da tsarin na kowane mutum ya kada kuri'a guda a zaben kasar na shekarar 2020 da ta 2021. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China