in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Najeriya ta daura damarar yaki da kalaman batanci
2017-08-25 09:39:17 cri
Mahukuntan Najeriya sun sha alwashin yaki da dukkanin kalamai wadanda ka iya rura wutar fitina tsakanin al'ummar kasar. Minista a ma'aikatar watsa labarai da al'adun Najeriya Lai Mohammed ne ya tabbatar da hakan, yana mai cewa za a hukunta dukkanin kafafen talabijin da radio da suka yada kalaman batanci a daukacin sassan kasar.

Lai Mohammed wanda ya bayyana hakan a birnin Abuja fadar mulkin kasar, yayin wani taron masu ruwa da tsaki da hukumar kula da kafafen watsa labaran kasar NBC a jiya Alhamis, ya ce wannan mataki daya ne daga manufofin da gwamnatin kasar ke dauka na dakile kalaman batanci.

Ministan ya kara da cewa, wasu daga kafafen Radio a fadin kasar na yada shirye shirye da ka iya rura wutar rikici, irin matakan da su ne suka kunna wutar kisan kiyashi da ya auku a kasar Rwanda cikin shekarar 1994, lamarin da ya haddasa kisan fararen hula har 800,000 cikin kwanaki 100 kacal.

Don haka sai ya ja hankalin hukumar NBC da kada ta yi kasa a gwiwa, wajen yaki da matsaloli masu alaka da yaduwar kalaman kiyayya a tsakanin al'ummar Najeriya.(Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China