in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ghana na shirin fafatawa da Congo a wasan neman gurbin shiga gasar cin kofin duniya
2017-08-31 10:53:27 cri

Kungiyar kwallon kafar kasar Ghana Black Stars, na shirye shirye gabanin fafatarwa da kasar Congo, a wasan neman gurbin shiga gasar cin kofin duniya daga bangaren kasashen nahiyar Afirka.

A shekara mai zuwa ne dai za a buga gasar ta cin kofin duniya, wanda hukumar FIFA ke shiryawa a kasar Rasha.

Tuni dai kocin Black Stars Kwesi Appiah, ya gayyaci 'yan wasa 24 domin karawar wadda za ta wakana a filin wasa na birnin Kumasi a ranar Juma'a, bayan kuma kwanaki 4 kasashen biyu su hadu a birnin Brazaville, domin buga wasa zagaye na biyu.

A wasan horo na ranar farko, 'yan wasa 11 sun taka leda karkashin kulawar koci Kwesi Appiah. Ana kuma sa ran ganin karin 'yan wasan da aka gayyata a raneku masu zuwa.

Kungiyar Black Stars dai na neman gurbin gasar cin kofin duniya a karo na 3 a jere, kuma a yanzu tana da maki daya a wasanni biyu da ta buga a rukunin E. A daya hannun kuma, Masar za ta kara da Uganda a wannan rukuni, a ranar 31 ga watan nan na Agusta.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China