in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kocin Namibia ya ce da ma ya yi hasashen samun nasara kan Zimbabwe
2017-07-20 10:25:13 cri
Kocin kungiyar kwallon kafar kasar Namibia Ricardo Mannetti, ya ce da ma can yayi hasashen samun nasarar da kungiyar sa ta yi kan takwararta ta Zimbabwe, bayan da kungiyoyin biyu suka tashi wasan su na ranar Lahadi, Namibia na da kwallo daya Zimbabwe na nema. Dan wasan Namibia Hendrick Somaeb ne dai ya zura kwallo daya tilo da aka ci a wasan, cikin minti na 47 da take wasa.

Cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Lahadi, Koci Mannetti ya bayyana farin cikin sa da wannan nasara, yana mai cewa ya ji dadi ganin yadda 'yan wasan sa ba su yi kasa a gwiwa ba, wajen jefa kwallon da ta ba su nasara a wasan da aka buga a gida.

Sai dai kuma ya ce, yanzu haka ba bu abun da ya rage masu illa maida hankali su ga sake samun nasara a wasa na biyu da za su buga a Harare fadar mulkin Zimbabwe a ranar 23 ga watan nan. Duk kungiyar da ta yi nasara a wasan na gaba, ita ce za ta kara da ko dai Comoros, ko kuma Lesotho, a zagayen karshe na neman gurbin shiga gasar cin kofin Afirka da za a buga badi a kasar Kenya.

Koci Mannetti ya sake jaddada kwarin gwiwar sa, game da lashe wasan na ranar Lahadi mai zuwa, yana mai cewa za su doke Zimbabwe wadda ita ce ta lashe kofin COSAFA da aka kammala gasar sa ba da jimawa ba.(Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China