in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin za ta samar da yanayin da ya dace ga harkokin kirkire-kirkire
2017-08-31 09:22:44 cri
Kasar Sin za ta bullo da wasu matakan yin gyare-gyare da nufin samar da yanayin da ya dace ga harkokin kirkire-kirkire da kuma raya kasa. An cimma wannan matsaya ce yayin taron majalisar zartaswar kasar na jiya Laraba da Firaminista Li Keqiang ya jagoranta.

Wata sanarwa da aka fitar bayan taron, ta bayyana cewa, an cimma wannan shawara ce, bayan nasarar da aka samu a wasu manufofin yin gyare-gyare na gwaji kan yadda za a inganta wasu hukumomi da yanayin kasuwannin masana'antu da bangaren kirkire-kirkire, inda mahalartar taron suka goyi bayan cewa, lokacin ya yi da za a aiwatar da wadannan gyare-gyare a kasa baki daya.

Sanarwar ta kara da cewa, idan har ana son a karfafa gwiwar harkokin da suka shafi kirkire-kirkire, to, wajibi ne a tallafawa kanana da matsakaitan masana'antu da kudade. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China