in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wata kotun Isra'ila ta tusa keyar iyalan Ba-palasdinan nan da ya halaka wasu iyalai a yammacin kogin Jordan
2017-08-28 10:05:01 cri
A jiya Lahadi ne, wata kotun soja a Isra'ila ta tusa keyar 'yan uwan Ba-palasdinan nan su biyar da ya kashe wasu mutane uku 'yan gida daya dake zaune a gabar yammacin kogin Jordan a watan Yulin da ya gabata.

Kotun dai ta yanke hukuncin cewa, 'yan uwan Omar al-Abed ciki har da iyayensa sun san abin da dan nasu yake shirin aikatawa, amma suka kasa sanar da mahukuntan kasar Isra'ila.

Ana zargin cewa Omar Al-Abed ya shiga gidan Halamish ne dake yammacin birnin Ramallah inda ya kashe iyalan uku ta hanyar daba musu wuka, ciki har da mahaifi da 'yarsa da kuma dansa guda.

A hannu guda kuma, kotun ta yanke wa mahaifin Omar din wato Abd al-Jalil hukuncin daurin watanni biyu a gidan yari. Mahaifiyarsa Ibtisam ta shaidawa manema labarai cewa, ta gamsu da hukuncin zaman gidan yari na wata guda da aka yankewa dan nata. Yayin da 'yan uwansa maza da kanwansa kuma aka yanke musu hukuncin zaman gidan yari na watanni takwas.

A ranar 16 ga watan Yulin da ya gabata ne dai, mahukuntan Isra'ila suka rushe gidan iyalan al-Abed mai hawa biyu dake kauyen Kobar a tsakiyar gabar yammacin kogin Jordan. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China