Abbas ya bayyana haka ne a yayin da yake ganawa da tawagar jam'iyyar New Moment ta kasar Isra'ila a jiya Lahadi a birnin Ramallah dake yammacin kogin Jordan.
A nasa bangare, shugaban jam'iyyar ta New Moement Zehava Gal-On ya ce, bisa matsayin su na abokan zaman lafiya, babu banbancin ra'ayi a tsakaninsu da shugabannin Falestinu, suna kuma dagewa ga manufar kawo karshen ayyukan mamaye, tare kuma da kafa kasa mai 'yancin kai, bisa iyakar kasa da aka shata a shekarar 1967.
Jam'iyyar New Moement na da sassaucin ra'ayi a Isra'ila, tana kuma dora muhimmanci kan wasu batutuwa da suka shafi tabbatar da zaman lafiya da Falesdinu, da kare hakkin bil Adama, da 'yancin addinai, da kiyaye muhalli da dai sauransu. (Bilkisu)