in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane fiye da 30 sun mutu sakamakon harin da aka kai wani masallaci a birnin Kabul na kasar Afghanistan
2017-08-27 13:41:11 cri
Hukumar kiyaye tsaro ta kasar Afghanistan ta ce yawan mutanen da suka mutu sakamakon harin da aka kai wani masallacin dake birnin Kabul ranar Juama'a da ta gabata ya zarce 30, yayin da adadin wadanda suka jikkata ya kai a kalla 80.

kafofin yada labaran kasar sun ruwaito cewa, wasu mahara ne suka kai hari masallacin mabiya darikar Shi'a dake unguwa ta 11 na arewacin birnin Kabul, a lokacin da jama'a da dama ke sallah.

Rahotannin sun ce mahara a kalla 4 ne suka kai harin, inda biyu daga cikinsu 'yan kunar bakin wake suka tada bam dake jikinsu a cikin masallacin, yayin da 'yan sanda suka harbi sauran biyun har lahira.

Shugaban kasar Afghanistan Ashraf Ghani da ya fitar da sanarwa a ranar, ya yi Allah wadai da harin, ya na mai bayyana shi a matsayin babban laifi ga jama'ar kasar .

Tuni dai Kungiyar IS ta sanar da daukar alhakin harin. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China