in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jerin hare-hare sun kashe mutane 12 a Afghanistan
2017-06-04 12:54:10 cri
An kai jerin hare-hare na bom a brnin Kabul, hedkwatar kasar Afghanistan, a jiya Asabar, lamarin da ya haddasa mutuwar mutane a kalla 12, tare da raunatar wasu 18. Wadan nan sun kasance manyan hare-hare karo na 2 da aka kai birnin, tun bayan harin ranar 31 ga watan Mayu.

Wani gidan telabijin din kasar Afghanistan ya ba da labarin cewa, ana samun tashin boma-boman ne a arewacin birnin Kabul. Sa'an nan wata majiya ta gayawa wakilin kamfanin dillancin labarai na Xinhua na kasar Sin cewa, wasu 'yan kunar bakin wake 3 su ne da hannu a kai hare-haren. An kai hare-haren ne, a lokacin da ake bikin jana'izar mutanen da suka rasa rayuka a zanga-zangar da ta gudana a birnin Kabul a ranar Jumma'ar da ta gabata.

Kafin haka, a ranar 31 ga watan Mayu, an kai hare-hare ta wasu motoci makare da boma-bomai a birnin Kabul, lamarin da ya yi sanadin rasa rayukan mutane a kalla 100, gami da raunatar wasu 600.

Ganin hakan ya sa jama'ar kasar damuwa sosai kan yanayin tsaro da ake ciki a hedkwatar kasar. Daga bisani a jiya Asabar, jama'ar birnin Kabul sun kaddamar da babbar zanga-zanga, inda suka bukaci gwamnatin kasar da ta dauki matakan da suka wajaba don tabbatar da kwanciyar hankali a kasar. Sai dai zanga-zangar a karshe ta rikide ta koma tarzoma, lamarin da ya haddasa mutuwar a kalla mutane 5.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China