in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sakatare Janar na MDD ya yi tir da harin da aka kai kan masu ibada a Afghanistan
2017-08-02 15:00:57 cri
Sakatare Janar na MDD Antonio Guterres, ya yi tir da kakkausar murya, kan harin da aka kai kan wani masallaci a birnin Herat na kasar Afghanistan, al'amarin da ya yi sanadin mutuwar fararen hula 29 tare da jikkata wasu da dama.

Cikin wata sanarwa, kakakinsa Staphane Dujjaric, ya bayyana hari kan fararen hula a matsayin take hakkin dan adam da dokar jin kai ta duniya.

Harin ya zo ne kwana guda bayan wanda aka kai kan ofishin jakadanci Iraqi dake Kabul, inda 'yan asalin kasar ta Afghanistan 2 suka muta yayin da wani guda ya samu rauni.

Antonio Guterres ya kuma mika sakon ta'aziyya ga iyalan wadanda harin ya rutsa da su tare da yi wa wadanda suka jikkata fatan samun sauki cikin gagagwa.

Har ila yau, ya jadadda goyon bayansa ga al'umma da gwamnatin Afghanistan. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China