in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
UNITA ta yi watsi da sakamakon wucin gadi na zaben kasar
2017-08-25 20:16:31 cri

Babbar jam'iyyar adawa ta Angola (UNITA) ta sa kafa ta shure sakamakon wucin gadi na babban zaben kasar na ranar Laraban da ta gabata da hukumar zaben kasar ta sanar a jiya Alhamis.

Wakilin jam'iyyar Jose Pedro Catchiungo ya bayyana a yau Jumma'a cewa, hukumar zaben ta yi kuskure kuma sakamakon da ta bayyana babu gaskiya a cikinsa.

Sakamakon babban zaben kasar na shekarar 2017 da hukumar zaben kasar ta bayyana dai na nuna cewa, jam'iyyar MPLA mai mulki ce ke kan gaba da kaso 64.57 cikin 100 na kuri'un da aka kada. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China