in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaba Al-sisi na Masar ya bukaci cikakken rahoto game da kokarin da ake na yaki da ta'addanci a kasar
2017-08-25 11:15:52 cri

Shugaban Masar Abdel-Fattah al-Sisi, ya umarci gwamnatinsa ta shirya rahoto kan irin kokarin da take na yaki da ta'addanci da tsattsauran ra'ayi.

Kamfanin dillancin labarai na MENA ya ruwaito cewa, Abdel-Fattah Al-Sisi ya bada umarnin ne a jiya Alhamis, lokacin da yake ganawa da firaministan kasar da kuma wasu ministoci a birnin Alkahira.

Shugaban ya bukaci a yi nazarin binciken da wasu ma'aikatu mabambanta suka yi a baya, domin mika su ga majalisar koli na yaki da ta'addanci da tsattsauran ra'ayi don taimakawa sabuwar majalisar da aka kafa wajen samar da ingantaccen tsarin yaki da ta'addanci. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China