in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Masar ta yi Allah wadai da babbar murya game da harin ta'addanci da aka kaddamar a Najeriya
2017-08-17 09:27:59 cri
A ranar Laraba kasar Masar ta yi Allah wadai da harin ta'addanci da aka kaddamar a Najeriya wanda ya yi sanadiyyar hallaka mutane 28, sannan ya jikkata wasu da dama.

Ma'aikatar harkokin wajen Masar ne ta bayyana hakan cikin wata sanarwa, inda ta nuna cikakken goyon bayanta ga gwamnatin Najeriya da al'ummar kasar a kokarin da suke yi na yaki da ta'addanci, kana ta bukaci kasa da kasa da su goyi bayan kokarin da Najeriyar ke yi wajen dakile ayyukan ta'addanci da masu tsattsauran ra'ayi.

Kasar Masar ta aike da sakon ta'aziyya ga iyalan wadanda harin ya rutsa da su, tare ta fatan samun sauki ga wadanda suka jikkata.

A ranar Talata ne aka kadddamr da tagwayen harin kunar bakin wake a jihar Borno dake arewa maso gabashin Najeriya, inda mutane 28 suka rasa rayukansu, wasu mutane sama da 80 suka samu raunuka. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China