in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sarkin Morocco ya jaddada muhimmanin nahiyar Afirka ga kasar sa
2017-08-21 09:55:02 cri

Sarkin Morocco Mohammed VI, ya bayyana irin muhimmancin da nahiyar Afirka ke da shi a manufofin gwamnatin sa. Sarkin wanda ke jawabi yayin bikin cika shekaru 64 da juyin juya halin kasar sa, ya ce martaba makomar nahiyar Afirka batu ne dake da matukar daraja a gare shi, duba da yadda kasashen nahiyar suka kasance masu tarihi, da al'adu, tare da makoma ta bai daya.

Sarkin ya kara da cewa, Morocco na bin manufofin hadin gwiwa da sauran kasashen Afirka bisa kyakkyawar fahimtar ta ga nahiyar, tare da fatan gudummawar ta za ta share fagen cimma burikan nahiyar, karkashin manufar cin gajiya tare.

A shekarar 2017, Morocco ta sake komawa cikin kungiyoyin hadin kan Afirka bayan shekaru 33 da ficewar ta. Tuni kuma kungiyar raya tattalin arzikin Afirka ta Ecowas ta amincewa kasar komen da ta nema.(Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China