in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
ECOWAS ta amincewa kasar Morocco ta zama sabuwar mamba
2017-06-06 10:51:24 cri
Kungiyar raya cigaban tattalin arzikin kasashen yammacin Afrika (ECOWAS) ta bayyana amincewa ga kasar Morocco don zama sabuwar mamba bayan da kasar ta mika bukatar hakan a lokacin taron koli na shiyya da aka gudanar karo na 51 a Monrovia, babban birnin kasar Liberia.

Kafafen yada labarai na cikin gida sun rawaito cewa, shugabannin kasashen mambobin kungiyar sun amince da bukatar da kasar Moroccon ta gabatar na neman zama sabuwar mamba a kungiyar.

Morocco, wadda take matsayin 'yar kallo a kungiyar ECOWAS, ta gabatar da bukatar neman zama mambar ne a hukumance a watan Fabrairu, wata guda bayan da kasar ta zama mamba a kungiyar tarayyar Afrika AU.

Masarautar ta arewacin Afrika tana da kyakkyawar alaka mai karfi da kasashen yammacin Afrika. Ta kasance babbar mai zuba jari a yammacin Afrika, kuma ita ce kasa ta biyu mafi girma dake zuba jari a nahiyar Afrika.

A shekaru masu yawa da suka gabata, Morocco ta rattaba hannu kan daruruwan yarjejeniyoyi wadanda ke da matukar tasiri ga karfafa dangantaka a tsakanin kasashen mambobin kungiyar ta ECOWAS 15.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China