in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasashen Morocco da Nijeriya sun yabawa nasarar da shirin shimfida babban bututun gas da zai hada kasashen yammacin Afrika ke samu
2017-03-17 09:45:12 cri
Kasashen Morocco da Nijeriya sun yaba da irin nasarar da ake samu, game da shirin hadin gwiwa dake tsakaninsu, na shimfida bubutun iskar gas da zai hada kasashen biyu tare da wasu kasashen yammacin Afrika.

Wata sanarwar da ofishin Sarkin Morocco ya fitar, ta ce yayin wata tattaunawa ta wayar tarho, Sarkin Morocco Muhammad na 6 da Shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari, sun bayyana gamsuwa da ci gaban da ake samu ta fuskar musayar bayanai da ayyuka da suka shafi muhimmin aikin.

A watan Decemban bara ne kasashen biyu, suka kaddamar da gagarumin aikin da zai mika ya tunkari Turai, wanda kuma ke da nufin samar da hadin kai tsakanin arewaci da yammacin Afrika, da ba su damar samun makamashi mai zaman kanta, da gaggauta aiwatar da ayyukan samar da lantarki da kuma inganta tattalin arziki da ayyuakan masana'antu.

Ba a sanya wani lokaci na fara aikin shimfida bututun ba, haka zalika ba a bayyana nawa aikin zai lakume ba, sai dai, an gudanar da wasu taruka biyu kan aikin a Morocco. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China