in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Masana: Ci gaban tattalin arzikin kasar Sin zai amfanawa nahiyar Afirka
2017-08-18 10:08:38 cri
Masaniyar tattalin arzikin Afirka dake aiki a Bankin Standard Chartered Razia Khan, ta bayyana cewa, bankin yana hasashen cewa, tattalin arzikin kasar Sin zai bunkasa a shekarar 2017 da muke ciki.

Khan wadda ta bayyana hakan yayin da take yiwa taron manema labarai jawabi game da bunkasuwar tattalin arzikin duniya, ta ce alamu na nuna cewa, ci gaban tattalin arzikin kasar ta Sin za ta haifar da bukatar kayayyaki, zai kuma yi babban tasiri ga kayayyakin da ake samarwa a nahiyar Afirka.

Khan ta kuma ce tasirin ci gaban tattalin arzikin kasar ta Sin a kan tattalin arzikin Afirka kuwa, zai haifar da karuwar bukatar kayayyaki daga nahiyar Afirka. Ta kuma yi hasashen cewa, za a samu karuwar rukunin Sinawa masu matsakaicin kudaden shiga, sakamakon bunkasar tattalin arzikin kasar ta Sin, da karuwar kudaden shiga da kuma bukatar kayayyaki dake karuwa. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China