in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasashen Sin da Amurka za su shirya taron tattaunawa na farko kan tattalin arziki
2017-07-11 19:20:37 cri
A yau Talata ne, ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin ta tabbatar da cewa, za a shirya taron tattaunawa zagaye na farko kan batun tattalin arziki daga dukkan fannoni a tsakanin kasashen Sin da Amurka a ran 19 ga watan a Washington D.C., fadar mulkin kasar Amurka.

Shugaban kasar Sin Xi Jinping da takwaransa na kasar Amurka Donald Trump ne suka tsai da kudurin shirya taron a yayin da suke halartar taron kolin kungiyar G20 a birnin Hamburg na kasar Jamus, Mr. Geng Shuang, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin ne ya shelanta labarin nan.

Mr. Wang Yang, mataimakin firaministan kasar Sin da Mr. Steven Mnuchin, sakataren kudi na kasar Amurka da kuma Mr. Wilbur Ross, sakataren kasuwanci na kasar Amurka ne za su jagoranci wannan taron tattaunawa cikin hadin gwiwa, inda bangarorin biyu za su yi musayar ra'ayoyin kan batutuwan da suke shafar tattalin arziki da cinikayya. (Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China