in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Xi da Trump sun tattauna game da taron G20 ta wayar tarho
2017-07-03 14:40:21 cri
Shugaban kasar Sin Xi Jinping da takwaransa na Amurka Donald Trump, sun tattauna ta wayar tarho a yau Litinin, inda suka yi musayar ra'ayoyi game dangantakar dake tsakanin kasashen biyu, da batun taron G20 dake tafe, sannan da batutuwan da suka shafi zirin Koriya.

A lokacin tattaunawar tasu, Xi ya nanata cewa, tattaunawar shugabannin biyu ta haifar da samun kyakkyawan sakamako wajen kara karfafa huldar dangantakar dake tsakanin kasar Sin da Amurka tun bayan ganawar da shugabannin biyu suka yi a Mar-a-Lago.

Haka zalika, an samu tsamin dangantaka tsakanin Sin da Amurka, kuma tuni kasar Sin ta riga ta bayyana matsayinta ga Amurkar, in ji shugaba Xi.

Shugaban kasar ta Sin ya nanata cewa kasarsa tana daukar batun kudurin Trump da muhimmanci musamman don tabbatar da cewa Amurkar za ta mutunta tsarin kasar Sin daya tak da ba shi muhimmanci.

Xi ya ce, kasar Sin tana fatan Amurka za ta kiyaye batun Taiwan bisa tsarin ka'idojin da suka dace da manufofin gwamnatin Sin daya taka da kuma mutunta yarjejeniyar dake tsakanin Sin da Amurka yadda ya kamata. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China