in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Palasdinawa zai kawo ziyara kasar Sin
2017-07-11 18:59:38 cri
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Geng Shuang ya shaidawa taron manema labarai a yau Talata cewa, daga ranar 17 zuwa 20 ga watan, shugaban Palasdinawa Mahmoud Abbas zai kawo ziyara nan kasar Sin bisa gayyatar takwaransa na kasar Sin Xi Jinping.

Mr Geng ya bayyana cewa, ziyarar da shugaba Abbas zai kawo ita ce ziyararsa ta hudu da ya kawo kasar ta Sin. Ana kuma sa ran yayin wannan ziyara zai tattauna da shugaba Xi da Firaminista Li Keqiang da kuma shugaban majalisar kafa dokoki ta kasar Sin Zhang Dejinag.

Bugu da kari, ana sa ran sassan biyu za su yi jusayar ra'ayoyi game da hadin gwiwar dake tsakaninsu, da batutuwan Palasdinawa da sauran batutuwan dake shafarsu.

Mr Geng ya ce kasar Sin tana goyon bayan gwagwarmayar Palasdinawa na neman hakkokinsu. Kuma kasar Sin a shirye take ta taka rawar da ta dace a kokarin da ake na yayata shirin zaman lafiya tsakanin Palasdinawa da Isra'ila. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China