in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Tawagar jiragen ruwan sojan kasar Sin ta kai ziyara a Tanzania
2017-08-17 12:42:11 cri
A jiya ne tawagar jiragen ruwan sojan kasar Sin ta isa birnin Dar es Salaam na kasar Tanzania, inda ta fara ziyarar sada zumunta ta kwanaki hudu a kasar .

A yayin bikin maraba da zuwan tawagar, jagoran tawagar, Shen Hao ya bayyana cewa, ziyarar za ta taimaka wajen karfafa fahimtar juna tsakanin rundunonin sojojin ruwa na kasashen biyu da zurfafa hadin gwiwa da zamunci a tsakaninsu, ta yadda hakan zai habaka hadin gwiwar dake tsakanin al'ummomin kasashen biyu.

A yayin ziyarar tawagar a kasar Tanzania, wakilan kasashen biyu za su yi shawarwari da mu'amala kan harkokin da abin ya shafa da gasa da atisayen hadin gwiwa da dai sauransu. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China