in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kungiyar kasashen gabashin Afrika ta nemi jama'ar Kenya dasu kaucewa tashin hankali
2017-08-13 13:00:02 cri
A ranar Asabar kungiyar raya cigaban kasashen gabashin Afrika IGAD ta bukaci al'ummar kasar Kenya da su kaucewa duk wani abu da ka iya wargaza zaman lafiya da kwanciyar hankalin kasar.

Babban sakataren kungiyar Mahboud Maalim, ya bukaci dukkannin bangarori masu ruwa da tsaki da su bi matakan da suka dace, da kuma yin amfani da hanyoyin da shari'a ta tanadar wanda ke kunshe cikin kundin tsarin mulkin kasar ta Kenya.

Sanarwar ta zo ne bayan barkewar tashin hankali a wasu sassan kasar ta Kenya, bayan da hukumar zaben kasar ta ayyana shugaban kasar mai ci Uhuru Kenyatta a matsayin wanda ya lashe zaben shugabancin kasar a daren Juma'ar data gabata.

Jim kadan bayan sanar da sakamakon zaben ne aka fara samun barkewar tashin hankali musamman a yankunan Kisumu da wasu sassan birnin Nairobi, inda 'yan adawa suka fi rinjaye.

A ranar Asabar, masu zanga zangar sun yi fito na fito da 'yan sanda a Kibera, inda aka dinga jin karar harbe harben bindigogi, kana an ga motocin daukar marasa lafiya na ta kai kawo a kan tituna.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China