in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gamayar jam'iyyun adawa na kasar Kenya sun bukaci hukumar zaben kasar ta bawia 'yan adawar nasara
2017-08-11 10:45:41 cri
Shugabannin gamayyar jam'iyyun adawar kasar Kenya, sun nemi hukamar zaben kasar da ta bayyana sakamakon karshe na zaben shugaban kasar, inda ta bayyana dan takararsu na jam'iyyar adawa Raila Odinga, a matsayin wanda ya lashe zaben na ranar Talata inda ya kada shugaban kasar mai ci Uhuru Kenyatta.

Shugaban hadakar jam'iyyun adawar kasar NASA, Musalia Mudavadi ya ce, sakamakon zaben dake cikin babbar na'urar adana bayanai ta hukumar zaben kasar, IEBC, ya nuna cewa, Odinga ne ya yi nasara a zaben da yawan kuri'u miliyan 8.4, inda ya dara Kenyatta mai kuri'un miliyan 7.75.

Ya ce wata majiya ce daga hukumar zaben kasar ta sheda musu sakamakon zaben a daidai lokacin da ake samun bayanai dake cin karo da juna, lamarin da aka iya jefa kasar cikin tashin hankali sai dai NASA ta ce wannan ba shi ne burinta ba. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China