in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Yayin wani samame a yankin Sinai, sojojin Masar sun kashe 'yan tada kayar baya 40
2017-07-26 10:13:39 cri
Sojojin kasar Masar sun kashe wasu 'yan tada kayar baya 40 a wani samame da suka kai mazauninsu dake lardin arewacin Sinai.

Cikin wata sanarwa da ya fitar jiya Talata, kakakin rundunar sojin kasar Tamer el Refai, ya ce sojoji sun kashe wasu muggan 'yan tada kayar baya yayin wani samame da su ka kai ta sama da kasa a biranen dake arewacin lardin Sinai da suka hada da Arish da Rafah da Sheikh Zuweid.

Har ila yau, ya ce an kuma damke wasu guda 5 yayin samamen.

Tun bayan hambarar da mulkin tsohon shugaba Mohammed Morsi da sojoji suka yi a shekarar 2013, Masar ke fama da matsalar rashin tsaro, galibi a lardin Sinai, al'amarin da ya yi sanadin mutuwar daruruwan jami'an tsaro (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China