in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilin Sin: Ya kamata a karfafa hadin gwiwa tsakanin kafofin watsa labarai na Sin da Afirka.
2017-08-15 11:03:37 cri
An yi wani taron musayar ra'ayi tsakanin kafofin watsa labarai na kasashen Afirka da na kasar Sin a birnin Johannesburg na Afirka ta Kudu a jiya Litinin.

Mahalartar taron sun hada da mataimakin babban daraktan ofishin watsa labarai na majalisar gudanarwar kasar Sin Guo Weimin, da jakadan kasar Sin dake Afirka ta Kudu Lin Songtian, da wakilan kafofin watsa labarun kasar Sin dake Afirka ta Kudu, da kuma wakilan kafofin watsa labaru 15 na kasashe daban-daban dake nahiyar Afirka.

Dangane da yadda za a zurfafa hadin gwiwa a tsakanin kafofin yada labaru na Sin da Afirka, mista Guo Weimin ya ce, ya kamata a karfafa fahimtar juna tsakanin kafofin watsa labarai na kasar Sin da na kasashen Afirka, tare da karfafa hadin gwiwar dake tsakaninsu, domin daukaka mu'amalar bangarorin biyu zuwa wani sabon matsayi. Sannan kuma, bangarorin biyu su bayyana ra'ayoyinsu yadda ya kamata a duniya bisa hadin gwiwa da mu'amalar dake tsakaninsu. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China