in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Firaministan Habasha zai ziyarzi kasar Sudan
2017-08-14 10:25:29 cri
Rahotanni daga kasar Habasha na fadin cewa, a ranar Talata ce ake sa ran firaministan kasar Habasha Hailemariam Desalegn zai jagoranci wata tawaga da ta kunshi ministoci da manyan jami'an gwamnatin kasar don kai ziyarar aiki ta kwanaki uku a kasar Sudan, a wani mataki na karkafa hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu.

Wata sanarwar da ofishin watsa labarai na fadar shugaban kasar Habasha ya fitar, ta ce, a yayin ziyarar ana sa ran Mr Desalegn zai tattauna da shugaba Omar al-Bashir na Sudan kan yadda jagororin biyu za su nazarci hanyoyin karfafa hadin gwiwar dake tsakaninsu da kuma batutuwan da suka shafi harkokin kasa da kasa da na shiyya-shiyya dake shafar muradunsu.

Sanarwar ta kara da cewa, firaministan na Habasha zai kuma gana da takwaransa na kasar Sudan Bakri Hassan Saleh da kuma mataimakin shugaban kasar Sudan Hassabo Mohamed Abdul-Rahman.

An kuma tsara cewa, Mr Desalagn zai gabatar da lacca game da yankin kahon Afirka a babban dakin taron kawance dake birnin Khartoum, fadar mulkin kasar Sudan. Daga bisani kuma zai halarci liyafar al'adu da za a shirya masa da dare, baya ga ziyartar wasu kamfanoni da zai yi a kasar ta Sudan. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China