in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Habasha: Yawan mutanen da za su bukaci tallafin abinci na iya kaiwa 700,000
2017-08-09 10:48:16 cri
Hukumar dake kula da ayyukan magance bala'u ta kasar Habasha ko NDRMC a takaice, ta ce yawan 'yan kasar da za su bukaci tallafin abinci sakamakon bala'in yunwa nan da karshen wannan shekara ta bana, na iya karuwa zuwa miliyan 8.5.

Yayin taron rabin shekara, game da nazarin halin da kasar ke ciki a wannan fanni, hukumar NDRMC ta ce adadin masu fama da yunwa a kasar zai iya karuwa daga mutum miliyan 7.8 zuwa miliyan 8.5 a nan gaba.

A farkon shekarar nan ta bana ne dai mahukuntan kasar ta Habasha suka bayyana cewa, mutane miliyan 5.6 na fama da kamfar abinci a kasar, kana bayan dan lokaci adadin ya karu zuwa mutum miliyan 7.2, kafin kuma a watan Yuni wannan adadi ya kai ga mutum miliyan 7.8. (Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China