in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin za ta yi yaki da laifuffukan hada-hadar kudi da ake aikatawa ta kafar Intanet
2017-08-11 10:12:21 cri
Kotunan kasar Sin sun mai da hankali kan laifuffukan hada-hadar kudi da ake aikatawa ta kafar intanet domin tsaftace ci gaban bangaren.

A cewar wani daftarin ka'idoji da kotun kolin jama'a ta fitar a jiya, dole ne a matsa lamba wajen yaki da batutuwan kafa gidauniyar tara kudi ba bisa ka'ida ba ta intanet, wanda su ne jigo wajen takaita matsalolin kudi.

Domin magance irin wadanan batutuwa, daftarin ka'idojin ya ce ya kamata kotuna su hada hannu da hukumomin yankuna domin kare wadanda ka laifuffukan ka iya rutsawa da su.

Ka'idojin sun kuma bayyana batutuwan da suka shafi karbar kafin alkalami ba bisa ka'ida ba daga al'umma ko kuma kafa gidauniyar tara kudi da sunan asusun ajiya.

Sun kuma yi bayani game da yadda za a tafiyar da karar da ta shafi rikice-rikicen kudi.

Sama da mutane 16, 400 ne aka gurfanar da gaban kotu bisa laifuffuka daban-daban da suka shafi hada-hadar kudi a shekarar 2016. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China