in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta karfara matakan tantance katunan fitar da kudade na bankunan ketare
2017-06-02 21:11:12 cri
Hukumar kula da harkokin musayar kudaden ta kasar Sin ta ce ta fara tattara bayanai game da yadda za a rika amfani da katunan fitar da kudade a ketare a wani mataki na yakar yadda ake halatta kudaden haram.

Wata sanarwar da hukumar kula da harkokin kudaden musayan ketare ta majalisar gudanarwar kasar ta fitar a yau Jumma'a, ta bayyana ceewa, daga ranar 1 ga watan Satumban wannan shekara, an bukaci bankuna da su rika bayar da rahoto game da kudaden da masu hulda da su suka cire da kuma duk wasu yarjejeniyoyin da aka kulla wadanda suka haura Yuan 1,000 da manyan shaguna, ko aka cire a ketare ta hanyar amfani da katunan cire kudade na bankuna.

Sanarwar ta ce, an dauki wannan mataki ne, domin inganta ayyukan bankunan da inganta muhimman bayanai game da kudaden da aka cire a ketare ta hanyar amfani da katunan bankuna ta yadda zai dace da bukatun hadin gwiwar kasa da kasa na yaki da halatta kudin haram, da katse kafofin da 'yan ta'adda ke samun kudade, da yaki da masu kin biyan haraji. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China