in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Zambia ya taya Kagame na Rwanda murnar lashe zabe
2017-08-10 09:12:05 cri
Shugaban Zambia Edgar Lungu, ya taya takwaransa na Rwanda Paul Kagame, murnar sake lashe zaben kasar da aka yi a makon da ya gabata.

Edgar Lungu ya ce sake zaben Paul Kagame alama ce dake nuna yakinin da al'ummar Rwanda ke da shi a kan shugabanci da manufofinsa ga kasar.

Wata sanarwar da ofishin shugaban kasar ya fitar ta ce Zambia na sa ran ci gaba da hada hannu da gwamnatin Rwanda wajen magance batutuwa da suka shafi kasashen biyu da kuma sauran kasashe.

Paul Kagame mai shekaru 59 da ya lashe zaben shugaban kasar Rwanda da gagarumin rinjaye, ya samu wa'adi na 3 kan mulki, inda zai dora akan shekaru 17 da ya yi yana jan ragamar kasar.

A cewar sakamakon da hukumar zaben Rwanda ta fitar, shugaban ya lashe zaben ne da kashi 98.79 na kuri'un da aka kada, inda ya samu kuri'u miliyan 6.6. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China