in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta nuna rashin jin dadinta ga Zambia kan batun kama Sinawa
2017-06-05 10:59:42 cri

A jiya Lahadi ne, ofishin jakadancin kasar Sin da ke kasar Zambia ya fitar da wata sanarwa game da batun Sinawa 31 da aka tsare a lardin Copperbelt na kasar, inda ya bukaci bangaren Zambia da ya saki Sinawan ba tare da bata lokaci ba. Kawo yanzu dai, ofishin jakadancin ya aika da ma'aikatansa don tattaunawa da mahukuntan na Zambia kan wannan batun, tare da ziyartar Sinawan da aka tsare.

A kwanan baya ne, hukumar kula da kaurar jama'a ta Zambia ta tsare Sinawa 31 da ke lardin Copperbelt bisa hujjar wai suna sayen danyun ma'addinin tagulla ba bisa doka ba.(Kande Gao)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China