in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin na fatan ganin Zambia za ta saki Sinawa ba tare da bata lokaci ba
2017-06-05 19:04:53 cri
Game da batun Sinawa 31 da bangaren 'yan sandan lardin Copperbelt na kasar Zambia ya tsare a kwanan baya, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Hua Chunying ta bayyana cewa, kasar ta za ta ci gaba da kula da wannan lamari, tana mai fatan Zambia za ta saki Sinawan ba tare da bata lokaci ba.

Madam Hua ta bayyana hakan ne a yayin taron manema labaru da aka saba yi a yau a nan birnin Beijing, inda ta jaddada cewa, har kullum gwamnatin Sin na bukatar kamfanonin ta da Sinawa dake kasashen ketare za su bi dokokin wurin da suke, kuma ba ta kare duk wani aiki da ya saba wa dokoki, amma kuma tana adawa da dukkanin wasu matakai na matsawa Sinawa dake ketare. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China