in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Boko Haram ta hallaka masunta 31 a arewa maso gabashin Najeriya
2017-08-09 09:40:53 cri

Gwamnan jihar Borno dake arewa maso gabashin tarayyar Najeriya Kashim Shettima, ya ce mayakan kungiyar Boko Haram, sun hallaka masunta a kalla 31, yayin wasu tagwayen hare-hare da suka kaddamar a garin Baga dake jihar Borno.

Gwamnan ya ce, mayakan kungiyar sun kai hare-hare a garin na Baga ne tsakanin ranekun Asabar da Lahadi, kuma bisa rahotanni da gwamnatinsa ke samu, har yanzu mayakan kungiyar na farwa fararen hula a sassan arewa maso gabashi, da yankunan tafkin Chadi mai makwaftaka.(Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China